IQNA

Mahatir Muhammad: Za Mu Ci Gaba Da Kare Batun Hakkokin Falastinawa

23:59 - February 29, 2020
Lambar Labari: 3484572
Tehran (IQNA) Firai ministan rikon kwarya na kasar Malaysia Mahatir Muhammad ya jaddada cewa ba za su kasa a gwiwa ba wajen kare hakkokin falastinawa.

Kamfanin dillancin labaran Anadolu ya bayar da rahoton cewa, a yayin da yake gabatar da jawabi a gaban taron Palestine a birnin Kualalampour, Mahatir Muhammad firai ministan rikon kwarya ya bayyana cewa, manyan kasashen duniya suna kauda kansu daga zalincin da yahudawa suke tafkawa a kan falastinawa.

Ya ce a duk lokacin da aka yi magana da al’ummar Falastinu da kuma zaluncin da yahudawan Isra’ila suke yi musu, sai manyan kasashen duniya su bata rai, tamkar cewa su Falastinawa ba mutane ba ne da suka cancanci su rayu kamar kowa.

Ya ci gaba da cewa, ko da wasa kasarsa ba za ta taba canja matsayinta na nuna cikakken goyon baya ga al’ummar falastinu ba, kamar yadda kuma za ta ci gaba da nuna adawa da duk wani mataki na danne hakkokinsu da zaluntarsu.

 

3882143

 

 

 

 

captcha